Ita rayuwa duk abinda kaga ya sameka daga Allah ne,sannan ba wani abu dake faruwa saida ƙudurar ubangiji,dan haka akan me zan saka wannan matsalar a cikin zuciya ta!bayan nasan shi Allah yana tare dani a kowane hali nike ciki kuma duk rintsi duk wuya bayan nasan shi kadai zai mani gata!yakike so inyi da wannan matsalar data zame mani abin shana ba dare ba rana?tunanin ki daukar mataki shine mafita ko kuwa in biyema yan uwana,makota da sauran jama’ar gari ina maida masu raddi akan kananun maganganun su da sukeyi akaina wadda ba abinda zata sauya daga cikin *Qaddarata* wadda ta dade da tabbatuwa a wajen ubangijina karfa ki manta Allah SWT da kanshi yace rubuta! sai *ALQALAMI* yace ya ubangijina me zan rubuta?sai Allah maɗaukakin Sarki yace duk abinda zaifaru na rayuwa daga samu rashi mutuwa arziƙi yawan mutanen da za’a halitta,na daga mutun ko aljan komai da kika gani Asma’u bai wanzuba saida Allah maɗaukakin Sarki ya kaddara shi tahanyar sa *ALQALAMI* ya rubutashi a Alon Lauhil Mahafus wanda ke cikin gidan Aljanna,inko har kema kinsan hakan mi zaisa in tadama kaina hankali akan rayuwa bayan nasan *Haka Allah Yaso* ya ganni tunda komai ya gama wanzuwa ta hanyar *ALQALAMI* ,saidai kisani hausawa nacewa bakin alqalami ya rigadata ya bushe amman ni nasan nawa bai bushe tunda bawa bai fidda rai daga rahamar ubangijin sa,addu’a na sauya kaddara cikin yardar Allah,wadda ita na maida ibadata a kowane lokaci Asma’u dan Allah kiyi hakuri kuma ki toshe kunnuwan ki,akan duk abinda zakiji kigani a cikin gari ba kanmu farauba kuma ba kanmu karauba,saukin ma ke Danginki da Yan uwanki basu saka maki idoba da har suke ganin son zuciya da ruwan ido su suka hanaki fidda miji wanda nawa Dangin ke ganin hakan akaina saidai abinda nasani koma minene Allah ya kaddara mani mijin da zan aura da ya’yan da zasuzo ta tsatsona harda jikokina duk yasa alqalami ya rubuta wannan tunkan asan za’a halicci ɗan Adam akan mi zan zauna intadama kaina hankali bayan nasan su masu yimani wannan surutun basu isa sukawo lokacin Aurena ba har sai Allah ya kaddara faruwar hakan sannan zanyi dan haka kawata kisa aranki komai *Lokacine* kuma yana nan zuwa kanmu tunda Allah yagama hukunta komai a cikin lauhil mahafus ta hanyar *ALQALAMI* .!”

zazzafan numfashi wadda na ambata da Asma’u ta furzar tana mai goge kwallan idanunta cikin kulawa ta kalleni tace.

“Hakane kawata kin kara mani hope da kika tunatar dani abun dana mance tabbas Allah yana taredamu duk runtsi duk wuya kuma shi zai mana gata a rayuwar mu,sannan komai lokacine Aure da haihuwa da mutuwa duk bawa bai gaggawar su,kuma bai jinkirin su da lokacin su yazo tabbas za’ayi dan haka nima nasama raina irin wannan hukuncin da kika yanke a cikin zuciyar ki Amina Allah yaimana jagorancin rayuwa.!”

Haka Asma’u ta ida maganarta cikin kunar rai dan lamarin yana tabama kawar tawa rai wanda ni awajena tun ina damuwa haryakai dana daina damuwa kwata kwata a cikin zuciya duk da bazance ban damuwaba saidai na rage kaso hamsin cikin ɗari,kama hannayen kawar tawa nayi nace.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *